A watan Agustan shekarar 2019, gwamnatin Najeriya ta rufe kan iyakokinta da wasu ƙasashe makwabta ciki har da Jamhuriyar Nijar da Jamhuriyar Benin. Wannan mataki a wancan lokaci an ɗauke shi ne domin yaƙi da fasa-kwauri, hana shigo da kaya ba bisa ƙa’ida ba, da kuma kare tattalin arziƙin cikin gida.
Bayan wannan tsawon lokaci da aka dauka na takaita zirga-zirga tsakanin wadannan kasashe, lamarin ya shafi kasuwanci, da mu’amalar jama’a da kuma rayuwar al’ummomin da ke zaune a kan iyaka.
Sai dai bayan wannan tsawon lokaci a kwanan nan gwamnatin Najeriya ta sanar da sake bude iyakokinta da wadannan kasashe biyu, a wani mataki na farfaɗo da kasuwanci, da ƙarfafa haɗin kai da kuma bunƙasa tattalin arziƙin yankin.
Ko yaya bude wadannan iyakoki zai amfani kasashen biyu?
Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.