Yadda Bude Kan Iyakokin Najeriya Da Jamhuriyar Benin Da Niger Zai Amfani Alummar Kasashen
A watan Agustan shekarar 2019, gwamnatin Najeriya ta rufe kan iyakokinta da wasu ƙasashe makwabta ciki har da Jamhuriyar Nijar da Jamhuriyar Benin. Wannan mataki a wancan lokaci an ɗauke shi ne domin yaƙi da fasa-kwauri, hana shigo da kaya ba bisa ƙa’ida ba, da kuma kare tattalin arziƙin cikin gida.Bayan wannan tsawon lokaci da aka dauka na takaita zirga-zirga tsakanin wadannan kasashe, lamarin ya shafi kasuwanci, da mu’amalar jama’a da kuma rayuwar al’ummomin da ke zaune a kan iyaka. Sai dai bayan wannan tsawon lokaci a kwanan nan gwamnatin Najeriya ta sanar da sake bude iyakokinta da wadannan kasashe biyu, a wani mataki na farfaɗo da kasuwanci, da ƙarfafa haɗin kai da kuma bunƙasa tattalin arziƙin yankin.Ko yaya bude wadannan iyakoki zai amfani kasashen biyu?Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.
Mene Ne Ya Fi Kawo Samu Tsakanin Sana’a Da Digiri?
An dade ana muhawara a tsakanin masu sana’a da masu digiri, musamman wadanda suka yi gam-da-katar suka samu ayyuka masu tasiri, kan abin da ya fi kawu samu.Ko wanne bangare yana da kwararan hujjoji; amma masu raba gardama sun ce akwai zabi na uku.Shin wanne zabi ne wannan?Abin da shirin Daga Laraba zai yi nazari a kai ke nan.
Shin Ko Dawowar Dimokradiyya Ta Samar Da Kyakkyawan Fata Ga ‘Yan Najeriya?
A farkon Jamhuriya ta Hudu a shekarar 1999, dawowar Najeriya mulkin dimokuraɗiyya ya haifar da babban fata a zukatan ‘yan ƙasa, inda mutane suka yi tsammanin ƙarshen mulkin soja zai kawo adalci, ci gaban tattalin arziƙi, tsaro, da shugabanci nagari da ke sauraron muradin jama’a. Jama’a sun yi imanin cewa za su sami ‘yancin faɗar albarkacin baki, ingantaccen zaɓe, aikin yi, da rage talauci ta hanyar shugabannin da suka fito daga zaɓin jama’a. A cigaba da kawo muku shirye-shirye gabanin muhawarar Daily Trust shirin Daga Laraba na wannan makon ya yi waiwaye ne don jin irin fatan da ‘yan Najeriya ke da su bayan dawowar Demokradiyya.
Yadda Tattalin Arziki Da Ababen More Rayuwa Suke A Farkon Jamhuriya Ta Hudu Da Kuma Yanzu
A shekarar 1999, lokacin da Najeriya ta sake komawa mulkin farar hula, tattalin arzikin ƙasa da kayayyakin more rayuwa na cikin wani yanayi na dogon mulkin soja. A wancan lokaci, masana da manazarta harkokin tattalin arziki sun bayyana cewa dogaro da man fetur ya yi wa ƙasar katutu, masana’antu da dama sun tsaya cik, kuɗin ƙasa ya raunana, yayin da rashin aikin yi da talauci suka yi ƙamari. Haka kuma, a cewar manazarta, kayayyakin more rayuwa kamar hanyoyi, da wutar lantarki, da asibitoci da makarantu sun lalace sakamakon shekaru na rashin kulawa.Yanzu kuma, bayan shafe fiye da shekaru ashirin da biyar da dawowar mulkin farar hula, ra’ayoyin manazarta sun kasu kashi biyu. Wasu na cewa an samu sauye-sauye a wasu fannoni na tattalin arziki da kuma gina kayayyakin more rayuwa, yayin da wasu ke jaddada cewa hauhawar farashi, da karyewar darajar naira, da wasu batutuwa da dama sun cigaba da yiwa kasar katutu.Ko yaya tattalin arziki da kayayyakin more rayuwa suke a lokacin da Najeriya ta dawo mulkin farar huka da kuma wannan lokaci?Wannan shine batun da shirin Daga Larba na wannan makon zai yi duba a kai.
Dalilan Da Suka Sa Matan Wannan Zamanin Ba Sa Son Talaka
A da soyayya na kafuwa ne sakamakon gaskiyar mutum, ko nasabarsa, ko tarbiyyarsa ko kuma riko da addininsa. Mace kan so saurayinta ko da kuwa ba shi da ko anini, a wasu lokutan ma ko da wani mai hannu da shuni ya fito takan tubure ta ki shi. Sai dai a wannan zamani mata da dama kan fito fili suna bayyana irin saurayin da suke so, a galibin lokuta mai abin hannu.Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari ne kan dalilan matan wannan zamanin na kin auren talaka.